08/07/2025
MAIGIDA,KA ZAMA HASKEN ZUCIYAR MATARKA
Aure fa ba ciniki ba ne, ba Kuma dauri bane awuya ,shi alaka ce ta soyayya da tausayi. Yana da matuƙar muhimmanci ga namiji ya fahimci cewa matarsa ba mai aikin gida ba ce kawai, ita wata abokiyar rayuwa ce da ta sadaukar da rayuwarta saboda kai kanka da iyalinka.
Ta bar gidan iyayenta ta biyo ka da don so da amana.
Tana jure wahala, ciwo, damuwa da gajiya domin ganin ka kasance cikin farin ciki.
Tana daukar nauyin tarbiyyar yaranku da kula da komai na cikin gida, ba tare da albashi ba, abunda take bukata kawai fatan kulawa da soyayya daga gare ka.
Don haka Ina kira ga mazaje:
Ku rika gaya masu kalmomin soyayya kamar irinsu "Na gode", "Ina alfahari da ke", "Allah ya saka miki da alheri". e.t.c
Ku tausaya musu idan basu da lafiya, ko sun gaji — ku taimaka musu, ku nuna musu damuwa.
Kada ku zamo masu tsauri ko fushi — ku zamo masu saukin fahimta da juriya.
Ka tuna da Annabi Muhammad(SAW ) ya kasance mafi kyawun miji, mai tausayi, mai wasa da iyalinsa, mai share hawayensu.
Mace na bukatar kulawa kamar yadda furanni ke bukatar ruwa. Idan ka kula da ita da tausayi da kalmomi masu daɗi, zaka girbi soyayya, kwanciyar hankali, da zaman lafiya a gidan ku.
Allah ya ƙara mana fahimta da zaman lafiya a cikin aurenmu.
Wani zaice shege don bashida matane kubarshi zaiyi ai!!😄😄
To Ina Addua
Nikuma Allah ya bani mata tagari 🤲🤲
Baffah Isa Bajoga ✍️