15/05/2026
YANZU-YANZU: Jam'iyyar APC Ta Ɗage Zaɓen Fidda Gwani Na ‘Yan Takarar Majalisar Wakilai Zuwa Ranar Asabar
Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sanar da ɗage zaɓen fidda ‘yan takarar Majalisar Wakilai na babban zaɓen 2027 zuwa ranar Asabar, 16 ga Mayu, 2026.
Sanarwar ta fito ne cikin wata takarda da Kakakin Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Felix Morka, ya sanya wa hannu a Abuja ranar 14 ga Mayu, 2026.
Jam’iyyar ta bayyana cewa duk sauran ranakun da aka tsara domin gudanar da zaɓukan fidda ‘yan takara na sauran muƙamai ba su sauya ba.
Sabon jadawalin zaɓukan fidda ‘yan takarar APC ya kasance kamar haka:
Zaɓen Fidda ‘Yan Takarar Majalisar Wakilai — Asabar, 16 ga Mayu, 2026
Zaɓen Fidda ‘Yan Takarar Majalisar Dattawa — Litinin, 18 ga Mayu, 2026
Zaɓen Fidda ‘Yan Takarar Majalisar Dokokin Jihohi — Laraba, 20 ga Mayu, 2026
Zaɓen Fidda ‘Yan Takarar Gwamnoni — Alhamis, 21 ga Mayu, 2026
Zaɓen Fidda Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa — Asabar, 23 ga Mayu, 2026
APC ba ta bayyana takamaiman dalilin ɗage zaɓen na Majalisar Wakilai ba, sai dai masu sa ido kan harkokin siyasa na ganin matakin na da alaƙa da shirye-shiryen cikin gida da kuma tabbatar da gudanar da zaɓukan cikin tsari da lumana.
Jam’iyyar ta kuma buƙaci duk masu neman takara da magoya bayanta su ci gaba da bin dokoki da ƙa’idojin jam’iyyar yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen zaɓukan fidda gwani na 2027.