14/08/2025
Naje ajiye su Umma ne a park zasu tafi garin Minna ita da Zainab kanwata bikin wasu family friends dinmu haka. Da can ni zan kaisu don Nima na halarci daurin auren amma sai ya kasance inada wasu commitments bazai yiwu naje ba yasa naje na ajiye su.
Na sauke su kenan Ina sauke jakukunan su, aka karba ana jerawa a mota Muna fira dasu haka. Umma tace "Haba Aminu, wannan bikin fa yakamata ace kana wurin. Muje mana ka kira Saif yazo maka da kaya ya tafi da motar kawai." Na ki yadda nace mata bazai yiwu ba su je kawai. Ina Shirin tafiya kenan sai wata mota ta tsaya. Wani mutumi ne yafara fitowa ya fidda jakukuna sannan wata kyakkyawar yarinya ta fito, da Gani kasan wannan Yar Hutu ce, ga kyau ga haske ga Kamala, na kasa dauke Ido akanta.
Naji Yana ce mata "Hajiya karama muje, yace seat biyu ne saura" sai tace masa "tohm, muje idan ba'a samu kowa ba sai na cike kudin kawai. Je ka Kai masu jakan". Zazzakar muryarta ta kusa tafiya da imani na, haka na tsinci kaina Ina murmushi kamar Dolo.
Umma tace "Aminu kana iya wucewa abunka ai ba Wani abunda zaka mana" Zainab ma haka tace. Na kalli yarinyar tana takawa a hankali har ta zagayo ta shiga motar ta gaida su Umma s**a amsa. "Driver har yanzu Babu Wani ko? Zo zan biya kudin mutum guda muje" Ina Jin haka naje dawuri na samu driver na bada kudin nace zani garin Minna Nima. Umma da Zainab duk mamaki s**ayi. "Aminu, haka zakayi tafiya baka shirya kaya ba?" Umma tace "Yaya lafiya kuwa? Kace fa bazaka ba" Zainab tace. "Ke banson shirme Ina ruwan ki?" Na mata tsawa tayi Shuru. "Umma zan San yadda zanyi idan nakai" na gyara zama na Ina hangota tana gaba Ina bayan ta. A Raina na Rantse duk inda zata zan bita har gidan da zata sauka.
An kusa tada mota kenan sai wata matashiya ta fito daga bayan motar da ta kawo ta da jariri a hannu. Tazo har inda take zaune ta Mika mata shi tace "Aunty ga Adnan, Allah ya kiyaye hanya. Daman dagangan naki fito dashi tunda Umma tace he shouldn't be exposed to breeze. Dan Allah cover him well, ki gaida