10/06/2026
𝐒𝐀𝐊𝐀𝐓𝐀𝐑𝐄𝐍 𝐊𝐀𝐑𝐀𝐌𝐀𝐑 𝐇𝐔𝐊𝐔𝐌𝐀𝐑 𝐙𝐀𝐑𝐈𝐀 𝐓𝐀 𝐁𝐔𝐊𝐀𝐂𝐈 𝐀𝐋’𝐔𝐌𝐌𝐀 𝐒𝐔 𝐌𝐀𝐘𝐀𝐑 𝐃𝐀 𝐇𝐀𝐍𝐊𝐀𝐋𝐈 𝐊𝐀𝐍 𝐌𝐔𝐇𝐈𝐌𝐌𝐀𝐍 𝐀𝐘𝐘𝐔𝐊𝐀𝐍 𝐆𝐔𝐃𝐀𝐍𝐀𝐑𝐖𝐀 𝐌𝐀𝐈𝐌𝐀𝐊𝐎𝐍 𝐒𝐇𝐈𝐑𝐘𝐄-𝐒𝐇𝐈𝐑𝐘𝐄𝐍 𝐓𝐀𝐋𝐋𝐀𝐅𝐈 𝐆𝐀 𝐌𝐔𝐓𝐀𝐍𝐄 𝐊𝐀𝐃𝐀𝐍
A yau, Sakataren Karamar Hukumar Zaria, Hon. Shuaibu Abdullahi (Mai Canter), karkashin jagorancin Shugaban Karamar Hukumar, Engr. Jamil Ahmad Muhammad (Jaga) ya karbi tawaga da mambobin Kungiyar Bachirawa Support Group daga Bayan Cinema a ofishinsa.
Kungiyar ta ziyarci Sakataren ne domin gabatar da koke-kokensu dangane da rabon tallafi da Kakakin Majalisar Wakilai, Governor Senator Uba SaniRt. Hon. Dr. Abbas Tajudeen, ya gudanar a Zaria.
Yayin da yake jawabi ga tawagar, Sakataren ya yaba da wannan kokari na Kakakin Majalisar, amma ya yi kira ga mambobin kungiyar da daukacin al’ummar Zaria da kada su dauki wadananan tallafin a matsayin ma’aunin ci gaba.
Ya jaddada cewa babban nauyin gwamnati shi ne samar da ci gaba mai daurewa da tsare-tsare masu anfani ga kowa da kowa, ba wai raba tallafi kadai ba wanda kan iya haifar da rarrabuwar kai da rashin gamsuwa a tsakanin jama’a.
Sakataren ya ce, “Wadannan tallafe-tallafe ba za su taba gamsar da dukkan al’ummar Zaria ba. Maimakon haka, za su iya haifar da rudani da kiyayya ga gwamnati domin wadanda ba su ci gajiyar shirin ba za su dinga zargin gwamnati. Hakikanin ci gaba shi ne lokacin da hanyoyi, asibitoci, makarantu, ruwa da wutar lantarki suke anfani ga kowa da kowa, ba ga wasu tsirarun mutane ba.”
Daga nan sai ya bayyana manyan ayyukan ci gaba da Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Dr. Abbas Tajudeen, da Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, s**a samar a Zaria karkashin gwamnatin APC.
Fannin Ilimi
• Aikin Zaria Education City mai darajar Naira biliyan 80, wanda zai kunshi jami’a, School of Health, cibiyoyin koyar da ilimi da nazarin shari’a, kwalejin noma da kiwon dabbobi, makarantar wasanni, kwalejin koyon sana’o’i da fasaha, cibiyar horas da shugabanci da cibiyar bunƙasa mata.
• Kaddamar da sabbin cibiyoyi a Nuhu Bamalli Polytechnic, haɓaka Federal College of Education, kafa College of Health Sciences, National Open University Campus da College of Legal Studies.
• Shirin tallafin karatu ga dalibai 30,000 wanda ya kai darajar Naira biliyan 5.
• Tallafin karatu cikakke ga ɗalibai 250 na NILEST.
• Gyaran makarantu firamare da sakandare guda 116.
• Gina sabbin dakunan kwanan ɗalibai maza da mata a NILEST.
Fannin Lafiya
• Gina da kaddamar da Asibitin Kwararru mai gadaje 100 a Zaria tare da goyon bayan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.
• Kammala cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko masu gadaje 20 da cibiyoyin koyon sana’o’i a Kakiyeyi, Gwargwaje Kufena, Jushi, Rubuchi, Yeskwake, Anguwan Kaya, Gabari da sauran al’ummomi.
Ababen More Rayuwa da empowerment:
• Gina da gyaran gadojin Agoro, Kofar Doka, Abba da Nagoyi.
• Gina kasuwar Zaria City Market mataki na daya da na biyu a Amaru.
• Gyaran Nasara Stadium da Malam Musa Hall.
• Raba taraktoci, takin zamani, motoci 117, adaidaita sahu 200 da babura 1,000 ga manoma, matasa da masu sana’ar sufuri.
• Tallafin kudi kai tsaye ga mutane 2,400.
• Bai wa matasa 800 da aka horar tallafin Naira 250,000 kowannensu.
• Bai wa kananan da matsakaitan ’yan kasuwa 1,600 tallafin Naira 100,000 kowannensu.
• Alkawarin samar da asusun Naira miliyan 100 ga wadanda s**a kammala koyon sana’o’i.
NASARORIN GWAMNA UBA SANI A ZARIA DA JIHAR KADUNA
Hanyoyi da Ababen More Rayuwa
• Kammala t**in Dogon Bauchi zuwa Kakiyeyi zuwa River Galma mai tsawon kilomita 35 a Karamar Hukumar Zaria.
• Kammala t**in karkara na Hanwa zuwa Agoro zuwa Hanga Ruga wanda ya kawo ƙarshen matsalar sufuri da aka dade ana fama da ita.
• Kammala ayyukan inganta titunan Magajiya zuwa Kasuwan Amaru da Audi zuwa Kano Road a Zaria.
• Kaddamar da aikin sake gina hanyoyin cikin Ahmadu Bello University masu tsawon kilomita 60 tare da magudanan ruwa, fitilun t**i da hanyoyin masu tafiya a kasa.
• Gudanar da ayyukan hanyoyi 78 masu tsawon kilomita 775 a kananan hukumomi 23 na jihar.
LAFIYA:
• Habaka cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 255 zuwa mataki na biyu a fadin jihar Kaduna.
• Sake gina manyan asibitoci guda 12 da kafa cibiyoyin ƙwarewa guda 23.
• Kaddamar da Asibitin Renewed Hope mai gadaje 100 a Zaria tare da ci gaba da ayyukan cibiyoyin kwarewa a Babban Dodo da Chikaji.
Wutar Lantarki da Ruwa
• Samar da transformers 600 da solar streetlights 10,000 a fadin jihar.
• Zaria, Sabon Gari da Kudan sun amfana da rabon transfoma da dama.
• Samar da megawatt 8 na wutar lantarki ga Ahmadu Bello University ta hanyar yarjejeniya da Hukumar Rural Electrification Agency a watan October 2025.
• Farfado da fannin ruwa ta hanyar shirin Naira biliyan 100 wanda ya hada da biyan bashin Naira biliyan 1.3 da dawo da wutar lantarki ga matatun ruwa.
Ilimi da Noma
• Gina sabbin makarantun sakandare guda 62.
• Samar da dakunan karatu 2,326 da kujeru 30,742.
• Ƙara kasafin kuɗin noma daga Naira biliyan 1.48 a shekarar 2023 zuwa sama da Naira biliyan 74 a shekarar 2025.
A karshe, Sakataren ya sake jaddada aniyar Karamar Hukumar Zaria karkashin jagorancin Shugaban Karamar Hukumar na ci gaba da goyon bayan manufofi da shirye-shiryen da ke kawo ci gaba mai ɗorewa ga al’umma maimakon waɗanda za su haifar da rarrabuwar kai. Ya kuma yi kira ga Bachirawa Support Group da sauran masu ruwa da tsaki da su rungumi manufar APC ta gina Zaria ta hanyar samar da hanyoyi, inganta lafiya, ilimi da wutar lantarki, wadanda su ne ginshika ci gaba na gaskiya.