Ashman

Ashman Be smart strong and gentle

07/07/2023

Abubuwa 5 da Suke janyo Bala'i Acikin Al'umma

Hadisi Ya Tabbata daga Abdullahi ɗan Umar (Allah ya ƙara masa yarda)

Yace Watarana muna zaune sai ga Manzon Allah (S.A.W) yazo wucewa, Yace " ya ku taron muhajirai! Akwai wasu abubuwa guda 5 idan al'umma s**a Jarabtu dasu!

Ina Roƙon Allah kada ku riske wannan Lokaci.

1⃣ Duk Al'ummar da s**a bayyana Alfasha! Tabbas zasu samu kansu cikin Annoba da yaduwar sabbin cututtukan da ba'a taɓa ganin su ba!

2⃣ Duk Al'ummar da suke tauye modu da sikeli! Tabbas zasu samu kansu cikin yanayi na fari (rashin ruwan sama), Tsadar Rayuwa da cutarwa daga azzaluman Shuwagabanni.

3⃣ Duk Al'ummar da s**a hana zakkar dukiyoyinsu! Tabbas Allah zai hanasu ruwan sama! Idan kaga Ruwa, an yine kawai saboda yara da dabbobi da suke rayuwa a cikinsu.

4⃣ Duk Al'ummar da s**a saɓa alkawarin Allah da Manzon sa! Tabbas Allah zai ƙasƙantar dasu a gaban abokan gabansu.

5⃣ Duk Al'ummar da Shuwagabaninsu basu hukunci da Littafin Allah, kuma suke chanza Abinda Allah ya sauƙar! Tabbas Allah zai sanya gaba, yaƙi da ganin Aibin Junansu a tsakaninsu.

Ibn Majah ne ya Rawaito Wannan Hadisin.

Dan Girman Allah acikin Waɗannan Abubuwa 5 wanne ne ba'a aikatawa a Nigeria? A hakan kuma muke jiran ganin dai dai

Telegram
👇👇
https://t.me/karatun_malaman_sunnah

07/07/2023

Matashi Don Mene Ne Kakeson Yin Aure ????

—Daga Ibrahim Y. Ibrahim

Aure abu ne mai kyau domin sunnar Manzon Allah (S) ne. Daɗin daɗawa muna ƙara godiya ga Allah ta’ala da yaba iyayenmu ikon haifemu ta hanyar Aure ba ta hanyar Zina ba‚ Allah ka tsare mu da faɗawa ga wannan hallaka. Ya kai matashi mai son yin Aure! Akan mene ne kakeson yin Auren? Da za a tara matasa a ƙalla mutum 1000 a masu wannan tambayar 850 cikin mutum 1000 ɗin nan. Amsar da za su bayar shi ne; Ina son nayi Aure ne domin na Huta da yin wanki‚ sannan zan kwanta a sabon katifa ga mayafi mai ɗimi‚ gashi zan huta da sayan abinci‚ za ta rinƙa dafawa‚ kuma zanzo da abokai muci abinci‚ sannan ga daren farko da zan raya sunna‚ sa an nan zansha magani kala-kala domin sai nayi sau kaza don Inason ta haihu da wuri‚ da dai sauran dalilai daban-daban da wasu daga cikin Matasa suke son suga sunyi Aure.

Na’am bance ka cire hakan a Zuciyarka ba‚ amma kasan da cewa matarka sunanta matarka ba baiwa bace‚ kuma kasan ita ɗin wurin samun Natsuwarka ne‚ sannan ita kaɗaice Allah ya yarje ma ka ka kusanceta yayin da kayi kanason biyan buƙatan ka‚ kuma ka samu lada in kabi yadda shri’a ta koyar. Ya kai matashi mai son yin Aure‚ ka taɓa yin wannan tunanin? Ya ya za ayi in nayi Aure na kula da karatunta matata? Ya ya za ayi in nayi Aure na kula da addinin matata? Ya ya za ayi in nayi Aure na kula da yanayin mutanen da matata take huɗɗa dasu? Ya ya za ayi in nayi Aure nayi ƙoƙarin biyan buƙatun matata na yau da kullum? Ya ya za ayi na kula da ƴan ƙananun haƙƙoƙin matata? Ya ya za ayi naba matata kulawa fiye da mahaifinta? Shin wai ina da hankalin da zan riƙe mace da suna Aure? Shin ina da hanyoyin samun 5/10? Shin in nayi Auren nasan akwai iya ranakun da ake aikata Sunna ɗin?

Shin nasan akwai addu’o‚in da ake karantawa in za a aikata sunnar? Shin in zan aikata sunnar nasan ƙa’idojin da addini Musulunci ya tanadar? Shin in matata ta Haihu ina tunanin ya ya za ayi na ba yaro/yarinyar tarbiya da ilimi domin na sauke haƙƙi

*new post
06/08/2022

*new post


Barkan mu dashan ruwa👋👋👋🍇🍉🍊🍊🍒🥕🍏
26/04/2022

Barkan mu dashan ruwa👋👋👋🍇🍉🍊🍊🍒🥕🍏

25/04/2022

Address

Gombe
Abuja

Telephone

+2347042771341

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ashman posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ashman:

Share