MR A1

MR A1 Hey ladys and gentlemen

09/08/2022

06/08/2022

Sheikh Bashir Ahmad Sani Sokoto Hafizahullah

13/06/2022
11/06/2022
07/06/2022

PDF MOON SIGHTING 🌙 VS MOON FIGHTING 🙅‍♂️ AND QUEST FOR UNITY.

01/06/2022

Sa’adu Bin Abu Wakkas. Kashi Na 1

Wane ne Sa’adu bin Abu Wakkas:

Cikakken sunan Sa’adu shi ne Sa’adu bin Malik, Abu Wakkas bin Uhaibin bin Abdulmunaf bin Zahrah, Al’amir Abu Is’hak Alkuraishiy Almakkiy. Kuma an haife shi ne a shekara ta 32 kafin Hijirar Manzon Allah (SAW) daga Makka zuwa Madina.Ya hada dangantaka da Annabi (SAW) ta wajen mahaifiyar Manzon Allah, Aminatu bintu Wahab, domin mahaifinta dan uwan Kakan Sa’adu ne. Domin haka ne Jabir (RA) ya ce: “Wata rana muna zaune tare da Manzon Allah (SAW), sai Sa’adu ya doso mu, sai Manzon Allah (SAW) ya ce: “Ga kawuna, wane ne a cikinku zai nuna min kawunsa?” Hakim ya ruwaito. Ana yi wa mahaifin Sa’adu wato Malik alkunya da Abu Wakkas, wanda shi ne dalilin da ake kiran Sa’ad da Sa’adu dan Abu Wakkas.

Yadda Sa’adu ya karbi Musulunci:

Sa’adu bin Abu Wakkas ya riga sahabban Manzon Allah da dama karbar Musulunci. Kuma ya bayyana abin da ya sa ya karbi Musuluncin cikin fadinsa: “Wata rana cikin mafarki na ga kaina a wani wuri mai matukar duhu inda ba na iya ganin komai da ke kusa da ni, sai wani haske na farin wata da na hango daga nesa.
Na nufi inda wannan haske yake domin in fita daga duhun da ya rufe ni, ina matsawa kusa da wannan haske, sai na hango Abubakar da Aliyu dan Abu dalib (Allah Ya yarda da su) tuni sun riga ni isa wurin wannan haske. Lokacin da na farka sai na yi tunanin wannan mafarki nawa a karshe na tafi ga Abubakar na nemi fassarar da mafarkina yake nufi. A nan Abubakar ya bayyana mini cewa ai Muhammad dan Abdullahi, amintacce shi ne (ya bayyana) yana kiran mutane zuwa ga wani sabon addini, wanda yake kore bautar gumaka.” Nan take Sa’adu ya yi imani da sakon da Manzon Allah (SAW) ya zo da shi, ya nufi gidansa (SAW) don don karbar Musulunci.

Sa’id bin Musayyib (RA), ya ce, na ji Sa’adu (RA), yana cewa: “Ba wanda ya Musulunta ranar da na karbi Musulunci, kuma har na yi mako guda. Ni ne na uku (a bayan Abubakar da Aliyu) cikin wadanda s**a Musulunta.” Buhari ne ya ruwaito.

Wannan ya nuna su Sa’adu ne s**a sha tsangwamar kafirai tun farkon bayyanar Musulunci, kuma a gabansu duk hukunce-hukuncen Musulunci s**a sauka, (Allah Ya kara masa yarda da sauran sahabbai).

Adawar mahaifiyarsa ga shigarsa Musulunci:

Mahaifiyar Sa’adu mai suna Hamnah ta fito ne daga kabilar Bani Umayya, kuma tana da daraja da shahara a cikin danginta da mutanen Makka. Wata rana sai ta riski Sa’adu (RA) yana karatun Alkur’ani cikin sauti mai sanyi, sannan ta gan shi ya tashi yana yin wata ibada bakuwa a gare ta. Don haka sai ta tambaye shi abin da yake yi. Sa’adu ya ce, ya karbi addinin da Annabi Muhammad (SAW) ne ya zo da shi. Kuma yana bukatar ita ma ta shigo wannan addini, duk da cewa a lokacin a cikin sirri ake karbar Musulunci.

Wannan al’amari ya fusatar da mahaifiyar Sa’adu, don haka nan take ta ce, ya yi watsi da wannan sabon addini ya koma zuwa ga abin da iyayensa s**a yi imani da shi kuma suke bauta mawa. Sa’adu ya shaku da mahaifiyarsa sosai kuma yana matukar girmama ta tare da kyautata mata, amma da ya dubi matsayin da ya samu kansa a ciki na zamansa Musulmi, kuma ya dubi umarnin mahaifiyarsa na ya kafirce, sai ya yanke shawarar ya bijire wa umarninta na ya koma bautar gumaka, alhali ya gamu da hasken Musulunci, imani ya ratsa shi. Mahaifiyar ta yi bakin kokarinta wajen maganganu da lalama da hikima, amma ta gaza shawo kansa kan ya fita daga Musulunci.

Da ta ga ta gaza shawo kansa ta hanyar lalama da jawo ra’ayi, sai ta fito masa ta hanyar barazana domin ta girgiza zuciyarsa. Ta ce, ba za ta sake cin abinci ba ko shan wani abin sha ba, har sai Sa’adu ya fice daga sabon addininsa. Idan kuma bai fita ba, to haka za ta ci gaba da zama cikin yunwa da kishin ruwa har ta mutu! Ganin mahaifiyar Sa’adu ta fara aiwatar da kudirinta na daina cin abinci ko shan abin sha, kuma hakan ya fara barazana ga rayuwarta, sai mutane s**a fara surutai ga Sa’adu kan rashin damuwa da halin da mahaifiyarsa take ciki. Sai jama’a s**a dauke shi zuwa ga mahaifiyar tasa domin ya ga matsanancin halin da ta shiga, ko ganinta zai karkato da hankalinsa ya bar Musulunci a warware wannan matsala.

Sa’adu ya gan ta ya nuna tausayarsa da damuwarsa a kan halin da mahaifiyarsa take ciki, amma sai karfin imaninsa ga Allah ya rinjayi wani tausayin na dan Adam. Don haka, sai ya ce: “Na yi imani da Allah, ya mahaifiyata! Da za ki samu rai guda dubu, kuma ki rika rasa ran nan daya-bayan daya (ta bin irin wannan hanya da kika dauko), ba zan sauya ra’ayina in fita daga addinin Allah ba! Saboda haka ko ki ci abinci, ki sha abin sha, ko ki ci gaba da kauracewa, wannan ba zai sauya ni ba!”

Da mahaifiyar ta ji wadannan kalamai na Sa’adu ta san cewa ba ya da niyyar rabuwa da imaninsa, tilas ta hakura ta ci gaba da cin abinci da shan abin sha k**ar yadda ta saba. Wannan abin da ya faru ya yi daidai da fadin Allah (SWT) cewa: “Kuma Mun yi wasiyya ga mutum (wasiyyar) kyautatawa ga iyayensa, kuma idan s**a tsananta maka domin ka yi shirka da Ni game da abin da ba ka da ilimi gare shi, to kada ka yi musu da’a. Zuwa gare Ni makomarku take, sannan in ba ku labari ga abin da kuka kasance kuna aikatawa.” (Ankabuti: 8).

Duk da cewa Hamnah mahaifiyar Sa’adu ta koma ci da sha k**ar yadda ta saba, amma ba ta hakura baki daya ba, game da kudirinta na ganin Sa’adu ya yi watsi da addinin Musulunci

Domin haka sai ta yi gayyar mutane masu yawa a kan su taimaka su k**a mata Sa’adu idan ya zo gida domin ta daure shi, a hana shi fita har karshen rayuwarsa. Sai dai da Sa’adu ya gano wannan shiri, sai ya kaurace wa gidan ya koma inda ya fito domin kauce wa tarkon dauri da aka shirya masa. Haka dai ta yi ta yin yunkuri domin raba Sa’adu da imaninsa da addininsa, wani lokaci cikin ruwan sanyi, wani lokacin kuma cikin barazana da tsanantawa, amma duk da haka Sa’adu bai yi watsi da addinin Musulunci ba, inda ya ci gaba da jure duk take-takenta da musgunawarta.

Copy

31/05/2022

Yadda tafiyar farko na jirgin Titanic dauke da fasinjoji ya kasance. Amsar Tambayar Nafisa Auwal Auwal

RMS Titanic jirgin fasinja ne na Burtaniya, wanda ke karkashin layin White Star Line, wanda ya nutse a Arewacin Tekun Atlantika a ranar 15 ga Afrilun 1912 bayan ta bugi wani dutsen kankara a lokacin balaguron farko da ta yi daga Southampton, UK, zuwa birnin New York.

RMS Titanic shi ne jirgin ruwa mafi girma da ke shawagi a lokacin da ta shiga sabis kuma na biyu na manyan jiragen ruwa uku na Olympics da ke karkashin Kamfanin White Star Line. Kamfanin jirgin ruwa na Harland da Wolff ne s**a gina ta a Belfast . Thomas Andrews, wanda shi ne babban hafsan sojan ruwa na tashar jirgin ruwa a wancan lokacin, ya mutu a cikin bala'in.

Jirgin ruwan Titanic ya samu albarkar manya da kuma shahararrun injiniyoyin fasaha da kere-kere na wancan zamani. Akwai mutum uku da s**a dauki nauyin zana tsari da kira da kuma yanayin rayuwar wannan jirgi. Na farko shi ne Lord Pirrie, wanda darakta ne a kamfanin Harland Wolff da White Star Line. Sai wani kwararren mai zanen jiragen ruwa mai suna Architect Thomas Andrews, wanda shi ne manajan kere-kere na kamfanin, wato Construction Manager kenan. Sai na ukun su mai suna Alexander Carlisle, wanda ya kasance babban manajan ma’aikatan kera jirgin ne baki daya (Shipyard General Manager).

A Ranar 10 ga watan Afrailu ne dai jirgin RMS ( Royal Ship Mail ) RMS ya tashi daga babbar tashar jirgin ruwan birnin Southampton na kasar Ingila don zuwa birnin New York da ke kasar Amurka. Da ya dauko hanya sai yayi zango a tashar jirgin ruwa na Cherbourg da ke kasar Faransa, inda ya kara daukan wasu fasinjoji. Bayan wannan tasha, ya sake dakatawa a tashar Queens Town ta kasar Ailand, nan ma ya kara wasu fasinjojin. Duk da cewa ba kai tsaye ya dauki mutane a wannan tasha ba, saboda nauyin jirgin da girmansa sun sha karfin gabar tekun. Don haka da yazo daidai tashar, sai aka saukar da kananan kwale-kwale, aka kwaso fasinjojin da suke son tafiya. Dubi yadda aka kera jirgin ruwan Titanic..

Daga wannan tasha ta Queens Town, jirgin bai kara dakatawa a kowace tasha ba, sai tafiya babu k**a hannun yaro. A wannan lokaci jirgin ya dauki mutane 2,227 ne; tsakanin matuka jirgin, da ma’aikata, da injiniyoyi da kuma fasinjoji. Shugaban matuka jirgin gaba daya shi ne Captain Edward J. Smith. Bayan haka, akwai babban daraktan kamfanin White Star Line a cikin tafiyar, wato J. Bruce Ismay, sai kuma wanda ya shugabanci kera jirgin baki daya, wato Thomas Andrews. Daga cikin fasinjojin da ke cikin wannan jirgi, akwai ‘yan kasuwa, da shahararrun ma’aikatan banki, da kuma kasaitattun masu kudin kasar Ingila da Amurka da kasar Ailand.

Kudin fasinjan da ke matakin farko, wato First Class, shi ne dala 4,350 ($4,350), wanda aka kiyasta kimarsa da kimar dala a shekarar 2008 ya kai dala 95,860 ($95,860).

Bayan ya kwashe kwanaki hudu yana tafiya dare da rana safe da yamma, a daren kwana na biyar ne Captain Edwards ya fara samun sakonni daga hanyar sadarwa ta rediyo dake jirgin, cewa akwai curin tsaunin kankara a gabansu, wato Iceberg. Amma sai bai damu ba. Ana cikin tafiya, sai ma’aikatan da aka wakilta su rika lura da tafarkin da jirgin ke bi, wato Lookouts, s**a hango wannan tarin kankara a gabansu. Nan take s**a sanar da masu lura da cibiyar sadarwa, inda su kuma s**a fara watsa sakonni kan wannan lamari. Captain Edwards na jin haka, sai ya bayar da umarnin cewa a rage Gudu, sannan a juya akala zuwa bangaren hagu.

To amma wannan bayani bai zo da wuri ba. Kafin su gama juya akala, nan take wannan tsaunin kankara ya gurji mazaunin jirgin daga kasa, wato Hull kenan. Hakan ya sabular da karafan da ke rike da mazunin jikin jirgin, inda ruwa ya fara shiga nan take babu kakkautawa. Lokacin da Captain Edwards ya ga haka, sai ya sa aka fara rufe farfajiyar kasan jirgin, wato wurin da aka tanada don zuba kayayyaki kenan. Amma saboda tasiri da karfin wannan ruwa da ya fara shigowa, kafin a rufe sauran, guda hudu daga cikinsu sun fara cikewa da ruwa. Wadancan bututu guda takwas da aka tanada don amayar da ruwa sai s**a fara aikinsu, inda s**a ta amayar da ruwan zuwa waje, ta baya. Sai dai kuma kash, saboda girman jirgin, da kuma yawan ruwan da ke tudadowa daga gaba inda aka samu huji, wadannan bututun amayar da ruwa sun kasa amayar da ruwan cikin lokaci guda.

Nan take kasan jirgi ya fara cikewa, sai cikin dakunan mutane, sai hawa na sama. Ana cikin haka sai jirgi ya fara nutsewa ta baya, saboda tasirin ruwan da ke makare a kasansa. Wannan tasa sai kan jirgin ya daga sama, inda a karshe ya tsage ko ya karye a tsakiya; bangaren bayan ya yi kasa cikin teku, kan kuma ya zauna a sama. Kafin lamarin ya kazance haka, nan take sun fara aikawa da sakonnin neman agaji. Ana cikin haka sai ga wasu jirage s**a kawo dauki. To amma saboda kananan kwale-kwalen ceto, wato Lifeboats, da jirgin ya ke dauke dasu basu kai yawan mutanen da ke cikin jirgin ba, haka wasu s**a nutse cikin ruwa, s**a mace. Wasu kuma aka ceto su da kyar.

Bayan an gama tsamo wadanda s**a mutu da masu rai, a karshe dai mutun 1,517 ne s**a mutu. Hakan ya faru ne a daren 15 ga watan Afrailu, 1912. Wannan shi ne mafi munin hadarin jirgin ruwa da aka yi a shekarar, kuma yana cikin hadarurrukan da aka yi da s**a haddasa sauye-sauye a dokokin tafiyar da jiragen ruwa na duniya, wato International Maritime Laws.

Daga cikin dalilan da aka ta cewa sun haddasa wannan hadari dai akwai yawan gudu. Wannan shi ne sak**akon da gungun masu bincike da kasar Ingila ta kafa ya tabbatar. Cewa jirgin na gudu ne fiye da kima, don haka ya samu matsala wajen juyawa a lokacin da aka hango wancan tsauni na kankara. Wasu masu binciken kuma s**a ce ruhin jirgin ne ke da matsala, wato Rudder kenan a turance. Shi wannan ruhi dai shi ne mai nuna wa jirgin ruwa inda zai dosa; k**ar dai kwakwalwarsa kenan.

Copy

Address

Bauchi

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MR A1 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share