K̇i̇ṅġ R҇a҇m҇a҇d҇a҇n҇

K̇i̇ṅġ R҇a҇m҇a҇d҇a҇n҇ We're welcoming for everyone

25/07/2022

An kashewa wata mata mijinta da dan
Uwanta da baban ta a yakin Uhud da
Labari yazo mata sai tace ya lamarin
Annabi (saw) ya kasance?

Aka ce mata yana lafiya sai tace a nuna
Mata shi da ta ganshi sai tace kowa ce
Irin masiface idan bakai ta shafa ba
Karama ce ya manzan allah (saw) ❤️❤️

Kaji soyayyar shugaban halitta mai ratsa
Zuciya (saw)

Sallallahu alaihi wasallam ❤️❤️❤️❤️❤️

Allah kaqara mana soyayyar fiyayyen
Halitta annabi muhammadu (saw)

Allahumma amen 🤲

24/07/2022

😂😂SHEHU JAHA DA WANI SAURAYI😂😂

An yi wani saurayi mai girman kai kuma kullum
yana ikirarin cewa, " SHI BABU WANDA YA ISA YA YAUDARESHI DUK DUNIYA " rannan kuwa sai s**a gamu da shehu, shehu ya ce, " yawwa, daman kai nake nema, kai ne kake cewa ba wanda zai yaudareka?" Saurayi ya ce, " eh ni ne, ko zaka jaraba mu gani? "Shehu ya ce, " eh, amma ina so ka dan jira ni anan zan je gida in dawo to a sannan ne zan gwada maka yadda ake yaudara! " saurayi ya ce, " to jeka kadawo, mu gwada . Shehu ya juya ya tafi.

Saurayin nan sai da ya yi wuni guda a tsaye yana ta jira shehu ya dawo amma shiru bai dawo ba. Duk ya gaji, sai lankwashewa yake a tsaye. Can sai abokansa s**a zo s**a ce, " af! Kai kuwa me kake anan a tsaye duk ka gaji haka? " Saurayi ya kwashe yanda s**a yi da shehu ya faɗa musu.

Sai s**a ce, " ayyah! Ayyah! Ai yau dai an
yaudareka! Wannan abinda shehu ya maka ita ce YAUDARA! Yanzu haka shehu ya tafi kauye shida iyalinsa a kan jaki
Saurayi ya juya gida cike da bakin ciki!

ABINDA LABARIN NAN YAKE KOYARWA
1 - kada ka zamanto mai girman kai.
2 - kada ka dauki kan ka cewa ka fi kowa a cikin
al'umma.
3 - sannan idan ka fahimci cewa wani ya fi ka
wani abu to kada ka yi jayayya da shi akan abin
musamman ma ilimi da dabarun zaman duniya...

AnasAnas Bin Mukhtar Anas Bin MukhtarhAnas Bin MukhtaraRamadan Bin Mukhtar Ramadan Bin MukhtarhRamadan Bin Mukhtar

24/07/2022

BAFULATANI DA PROFESSOR



Profesa yaceidan nayi maka tambaya baka amsa ba zaka

bani 5000. Idan kuma kayi min tambaya
bansaniba zan baka 20000. professor ya
tambayi bafulatani "nawa ne nisan sama
zuwa kasa?" Bafulatani yace bai sani ba.
Bafulatani ya ba da 5000. Bafulatani yace
saura ni."Wace dabba ce idan tana kasa tana
da kafa 4 idan ta soma tashi tana da kafa 3
idan tayi sama sai ta koma kafa 2 idan ta
tashi saukowa sai ta sauko da kafa 1?"
Profesa ya zaro 20000 ya bayar dan bai sani
ba. Bafulatani zai tafi sai profesa yace
"menene ansar?". sai bafulatani ya zaro
5000 ya karawa profesa yace

NIMA BAN SANI BA

24/07/2022

RASHIN LAFIYAR SHEHU

Shehu jaha yayi rashin lafiya aka kwantar dashi a
asibiti, kasancewar sa mutun ne mai jama’a yayi ta
samun alheri daga wurin jama’a masu zuwa gaisheshi.
Sanadiyar haka daShehu ya samu sauki kullum in likita
yayi niyyar sallamarsa sai yace “hum humm likita ni
kawai nake jin abin da nake ji, to daman gadaje hudu
ne a jere, washe gari sai mai gadon farko ya mutu,
washe gari na gefensa ma ya mutu, washe gari daman
shehu shine a gado na uku, ya zaga k**a ruwa a ban
daki ya dawo, sai ya tarar da na gado na hudu shima
ya cika, sai Shehu yace to layi take bi kenan bata same
ni bane shi yasa ta wuje, tunda ta kure layin to lallai
zata dawo. Nan take bai jira likita ba, ya tattare
kayansa ya gudu.

Anas Bin Mukhtar
Ramadan Bin Mukhtar

24/07/2022

MUTUWAR SHAHADA

Wata rana Shehu ya tara almajiransa yana koya musu karatu aka falalar mutuwar shahada, ya bayyana masu cewa “duk inda wani ya kashe ka bisa kokarin kare dukiyarka, ko mutuncinka ko na iyalinka to kayi shahada”.

Kwatsam! sai wata rana rikici ya hada Shehu da wani ai kuwa sai wancan abokin fadan nasa ya biyo shi a guje da takobi tsirara. Ganin haka Shehu ya ranta a na kare, sai ko aka samu akasi hanya ta biyo da su ta makarantar almajiransa. Ai ko sai s**a ta cewa Shehu “malam ka tsaya kayi mutuwar shahada” amma ina bai yi ta tasu ba.

Gari da ya waye da yazo makaranta sai ya ce wa almajiransa yau zamuyi darasi ne akan FALALAR GUDUN CETON RAI!!!

24/07/2022

004. LABARIN TAJIRI DA IFRITU

Tsoho Na Biyu Mai Karnuka.

Daga nan sai tsoho na biyu mai karnuka ya matso wurin Ifiritu, ya ce ni ma ina da labarin da zan baka akan wadannan karnuka da kake gani, amma sai idan za ka ba ni sulusin jinin wanan mutum. Ifiritu ya ce, fadi labarinka mu ji. Tshoho mai karnuka ya fara labarinsa k**ar haka:

Tsoho na biyu ma’abocin karnuka ya matso kusa da ifiritu ya fara bayar da labarinsa, ya ce, ka sani ya kai shugaban sarakunan aljanu, wadan nan karnuka biyu ‘yan uwana ne, ni ne na ukunsu. Mahaifinmu ya mutu ya bar mana gadon dinari dubu uku. Da aka raba wadan nan kudi aka ba wa kowa nasa, sai ni na bude rumfa a kasuwa ina ciniki a cikinta, ina saye ina sayarwa. Yan uwana kuwa s**a tafi fatauci.
Bayan shekara guda, sai yan uwan nan nawa s**a komo daga fatauci, babu komai tare da su na daga dukiya, duk sun salwantar da ita. Na ce da su, “Ya ‘yan uwana ashe dama ba sai da na ba ku shawarar kada ku tafi fataucin nan ba?” Su ka ce da ni, “Ya dan uwanmu ashe baka yarda da kaddarar Allah mai girma da daukaka da ya yi nufi akan mu ba?”

Na karbe su. Na rike su, na tafi da su gidana, na ba su abinci da sutura mai yawa, sannan na tafi da su zuwa ga rumfata ta kasuwa na ce da su na yarda su zauna mu yi kasuwanci tare da su, duk ribar da aka samu a raba ta uku dai dai, kowa ya dauki kashi daya.
Mu ka zauna akan haka har zuwa wani zamani mai tsawo. Sai wata rana ‘yan uwan nan nawa s**a ce suna so za su koma fatauci tunda yanzu sun sami nasu jari, s**a kwadaitar da ni akan mu tafi tare domin an fi samun riba mai yawa a fatauci. Na ki amincewa da in bar rumfata saboda na san ina samun riba sosai a cikinta.

‘Yan uwan nan nawa ba su gushe ba suna kwadaitar da ni akan zuwa fatauci har tsawon wasu shekaru. Daga karshe dai s**a shawo kaina na amince da za mu tafi tare da su. Muka kidaya kudin da ke gare mu, muka ga muna da dinari dubu shida. Na ba da shawarar mu raba kudin nan biyu, mu bisne rabi a kasa mu tafi da rabi, koda tafiya ba ta yi kyau ba, ida

24/07/2022

WANNAN YA ISHE KI DARASI SHIGEN KI NA SU WAYE NE?

Kullum ga ki cikin kwalliya da turare mai daukar hankali, kinyi gyare gyare a jikin ki, kin sha magani, kin yi dilka, kinyi bleaching, kinyi Komi na gyaran jiki, kin sanya tufa yadda maza ke so, kuma kullum suna binki amma cikin su gaba-daya babu mai zancen aure, kowa sai yazo kuyi ta soyayya ya kashe miki kudi iya kudi, wani kudin ma ya kai a auri yanmata biyu ko uku, daga karshe sai ya kawo miki bukatar sa na ku saɓawa ALLAH, wani ko kai tsaye ma zai zo miki da buƙatar hakan!

Me ya janyo hakan? Shigar ki ce ta nuna tallar gabobin jikin ki k**e, kiji tsoron ALLAH, ki daina, sai ance kiyi aure sai ki fara cewa Wallahi duk mazan ne ba aure ke kawo su ba yan soyayya ne babu aure a lamarin su maza yanzu sun iskancs, ke kinyi shiga na kirki da ya dace namiji ya aure ki ki haifa masa ya'ya? Kiyi tarbiyyar su? Ke Kin zamo na kirki ?, kin yi shiga na kirki da namiji zai aure ki yayui alfahari ace wance mai shiga irin kaza ce fa wa-ne zai aura mai hali irin kaza ce fa?

Ke ga ki da anko zuwa Wancan bikin zuwa wannan, ga ki acan ga ki anan party, wa'ne saurayin ki, wa'ne kunje shan ice cream, wa'ne BESTY ? waye zai yarda ya aure ki?

Idan kina cewa ai ke ba fasika bace ba, ba za'a yarda ba saboda kin siffantu da siffar su kina yawo tamkar tsirara mu'amula da maza, ko ba kiyi za'a ce kina yi, kuma yau da gobe ke ba dutse bace matukar kika ci gaba da irin haka wataran za'a samu mai rinjayar dake cikin harkar banza shine gaskiyar magana kuma halayyar ki da shigar ki sun fi kusanta da Ɗabi'ar Mutanen banza, aukawa shine kika fi kusa dashi,

matukar akwai imani a kirji to tabbas za'a kalle shi a zahiri.

Kiji tsoron ALLAH ki tuba ki gyara dabi'un ki yar'uwa, domin dacewa duniya da lahira

Anas Bin Mukhtar
Ramadan Bin Mukhtar

ILIYA DAN MAI KARFI(1)ABIN   AL AJABIA wani gari can cikin kasashen Gabas, an yi wani ana kiransa Sahabi, da matarsa wai...
24/07/2022

ILIYA DAN MAI KARFI(1)

ABIN AL AJABI

A wani gari can cikin kasashen Gabas, an yi wani ana kiransa Sahabi, da matarsa wai ita Murjanatu. Suna zaune cikin gidan gona. Ba wadansu wadatattu ba ne sosai, amma kuma ba matalauta ba ne. Suna da yan dabbobi da gonaki. Abin da dai ya rage musu jin dadin zaman duniya shi ne rashin magaji kawai. Allah bai nufe su da samun da ba.

Shekara da shekaru suna ta neman haihuwa, amma ba su samu ba. Ran nan kwanci tashi, sai Murjanatu ta sami ciki. Wai kada ka so ka ga irin murnar da Murjanatu da Sahabi s**a yi. Tun cikin yana da wata hudu, Sahabi ya soma tanadin iccen biki.

Ran nan da rana tsaka, Sahabi yana aiki a bayan gida, cikin gona, sai ya ji an rafsa guda, Ayyururui! Ayyururui! , har sau uku. Sahabi ya jefad da fartanya, ya sheko da gudu cikin gida. Da zuwansa kuwa ya tarar da abin da ya ke fata ya gani. Murjanatu ta sauka, ta sami da, namiji, santilo. Da ranar ta kewayo, jama a s**a taru, aka rada wa jaririn suna Iliya.

Ana nan har yaro ya kusa isa yaye, sai rashin lafiya ya same shi, kafafuwansa duka biyu, da hannu guda, s**a shanye. Shi ke nan ya zauna a haka, har ya girma. Daga kan dan gadonsa ba ya iya fita ko ina, sai dai am fita da shi. Iyayensa s**a yi bakin ciki kwarai, s**a hakura.

Wata rana iyayen Iliya sun tafi gona, ba kowa gidan sai shi kadai, kan gadonsa, yana ta tunanin yadda duniya ta ke, yan kulle-kullen abubuwan da zai yi, da yana da kafafu. Kwanfa, sai ya ji an yi sallama, Salamu alaikum, salamu alaikum! Sai Iliya ya amsa, Alaikas salamu. Kowane ne ya shigo! Sai ga wadansu mutane su uku, suna sanye da tufafi irin na aLarabawa, sun yi shigar alhazai. Ko wannensu yana rike da doguwar tasbaha, yana ja. S**a zauna. Iliya ya yi musu maraba, s**a amsa masa da murna.

Iliya ya dubi mutanen nan da kyau, ya ga ba irin mutanen da ya saba gani ba ne. Sai ya zaci ko irin mutanen nan ne da ya kan ji ana cewa suna bi gari gari sun

Address

Jos

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when K̇i̇ṅġ R҇a҇m҇a҇d҇a҇n҇ posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share