Lukman Haske Enterprise/ Wearble, Shoes

Lukman Haske Enterprise/ Wearble, Shoes Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Lukman Haske Enterprise/ Wearble, Shoes, Clothing (Brand), Shop No, 103&51 Shendam motor part ahmadu bello Way Jos ( Bayan banki market), Jos.

18/08/2026

Haihuwar Manzon Allah SAW

An haifi Manzon Allah SAW ranar litinin 12 ga watan Rabi'ul Awwal a shekarar giwaye.

A daren da aka haifi Manzon Allah SAW, abubuwan mamaki sun bayyana. Daga cikin su akwai:
Kakkaryewar gumaka duk s**a faɗi akan fusakun su. Haske ya bayyana a tare dashi kuma wannan hasken seda ya haska benayen sham, kuma katangun Kisra ta tsatstsage kuma wutar da suke bauta ta mutu alhali bata taba mutuwa ba kafin lokacin, hakanan ƙoramar sawata itama ta qafe.

Ibn Abbas yace: An haifi Manzon Allah SAW ranar litinin, an aiko shi da Manzonci ranar litinin kuma yabar Makkah zuwa Madinah ranar litinin kuma yayi wafati ranar Litinin kuma ya ɗaga dutsen Aswad ranar litinin kuma an haifeShi da shayi kuma cibin sa a yanke SAW babu ƙazantar haihuwa a tare dashi se haske da ya haskaka ko ina.

18/08/2026

Tasowar Manzon Allah SAW

Manzon Allah SAW ya rayuwa maraya domin tun yana ciki Mahaifinsa ya rasu. Sai Kakan sa Abdulmuɗallib yacigaba da rainon sa.
Lokacin da Manzon Allah SAW yakai shekara shida, sai Mahaifiyar sa Nana Aminah ta tafi dashi Madinah dan su xiyar ci kawunnan sa ƴan Banun Najjar, ta zauna tare dashi a Madinah tsawon wata ɗaya, a tare da ita akwai Ummu Aiman.

Mahaifiyarsa tayi rashin lafiya a hanyar su ta dawowa daga Madinah xuwa Makkah sai ta rasu aka birne ta a wani qauye da ake kira Abwab. Sai Ummu Aiman ta dawo dashi Makkah wurin kakansa Abdulmuɗallib.

Da Manzon Allah SAW yakai shekara 8 sai Kakansa Abdulmuɗallib ya rasu, Sai Kula dashi yakoma hannun Baffansa (Dan uwan mahaifin sa) Abu-Ɗalib da wasiyyar Kakansa. Abu-dalib ya zamo yana kare shi daga dukkan cutarwar maqiya.

Lokacin da yakai shekara 12, sai duka tafi Sham domin kasuwanci, sai wani Malamin Nasara yace ma Abu-ɗalib ya maidashi Makkah saboda tsoron kar Yahudawa su cutar da Manzon Allah SAW.

An ruwaito cewa: Abu-Dalib ya kasance talaka sosai, sai Allah ya azurta shi albarkacin rainon Manzon Allah SAW da yakeyi a gidan sa.

Address

Shop No, 103&51 Shendam Motor Part Ahmadu Bello Way Jos ( Bayan Banki Market)
Jos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Lukman Haske Enterprise/ Wearble, Shoes posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share